fidelitybank

Isra’ila ne suka kashe ƴar Jaridar AlJazeera – MDD

Date:

Majalisar Dinkin Duniya ta tabbatar da cewa sojojin Israila ne suka kashe sanannar yar jaridar gidan talabijin na Aljazeera, Shireen Abu Aqla.

Mai magana da yawun Majalisar ta ce wani bincike mai zaman kansa da suka gudanar kan harbin na 11 ga watan Mayu ne ya tabbatar da hakan. In ji BBC.

An kashe Shireen yayin da take kawo rahoto kan ayyukan Israila a Gabar Yamma da Kogin Jordan da Israila ta mamaye.

Kuma tun a lokacin ne Falasdinawa da gidan jaridar na Aljazeera suke zargin dakarun Israila da harbe ta da gangan.To amma Israila ta ce ya yi wuri a iya zarginsu da aikata kisan.

Duniya ta yi tir da kisan yar jaridar mai shekaru 51, duk da tana sanye da rigar kariya daga harsashi, da kuma hular kwano da ke nuna alamun cewa yar jarida ce.

Da take magana da yan jarida a Geneva, Ravina Shamdasani ta ce Ofishin Kare Hakkin Bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya ya gano cewa ” harsashin da ya kashe Abu Aqla da wanda ya jikkata abokin aikinta Ali Sammoudi ya fito ne daga dakarun Israila”.

”Harsashi biyu aka harbo, inda daya ya jikkata Ali Sammoudi a kafada, yayin da daya ya shiga kan Abu Aqla ya kuma kashe ta nan take”, in ji ta.

Sai dai Israila ta ce tana kan gudanar da nata bincike kan kisan, kuma duk da ta gano cewa harsashin bindigar soja ne ya yi harbin, to amma tana bukatar a bata harsashin da ke hannun Falasdinu don ta kammala binciken.

To amma gwamnatin Falasdinu ta ce ba zata bada harsashin ba don bata amince da Isra’ila ba.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Duk wani tuggun ku Atiku da El-Rufa’i ba za ku iya kayar da Tinubu ba – Bwala

Fadar shugaban kasa ta yi watsi da kokarin da...

Mutuwar Dantata ta girgiza kasa baki daya – Tinubu

Shugaban kasa Ahmad Bola Tinubu ya bayyana Alhaji Aminu...

Wike ya caccaki Rotimi a kan jam’iyyar ADC

Ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, ya caccaki tsohon...

Tsige ni daga mukamin Wazirin Gaya ba a kan doka ba ne – Usman Alhaji

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Kano, Alhaji Usman Alhaji, ya...

Gini mai bene uku ya danne Mutane a jihar Legas

Wani gini mai bene uku ya rufta a unguwar...

Kotu ta daure Matashi dan Tiktok da ya ke sanya rigar mama

Wata kotu a jihar Kano, ta yanke wa wani...

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun...

Dan wasan Liverpool Diago Jota da Kaninsa sun mu a hadarin mota

Ɗan wasan ƙwallon ƙafar Liverpool kuma ɗan ƙasar Portugal,...

Mun shirya tunkarar APC a 2027 – ADC

A ranar Laraba ne manyan ƴan adawar siyasa suka...

Mun dagulawa Iran lisafi na tsawon shekaru biyu a nukiliyar ta – Amurka

Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce bayannan leken asirinta ya...

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...
X whatsapp