fidelitybank

Isra’ila ne suka kashe ƴar Jaridar AlJazeera – MDD

Date:

Majalisar Dinkin Duniya ta tabbatar da cewa sojojin Israila ne suka kashe sanannar yar jaridar gidan talabijin na Aljazeera, Shireen Abu Aqla.

Mai magana da yawun Majalisar ta ce wani bincike mai zaman kansa da suka gudanar kan harbin na 11 ga watan Mayu ne ya tabbatar da hakan. In ji BBC.

An kashe Shireen yayin da take kawo rahoto kan ayyukan Israila a Gabar Yamma da Kogin Jordan da Israila ta mamaye.

Kuma tun a lokacin ne Falasdinawa da gidan jaridar na Aljazeera suke zargin dakarun Israila da harbe ta da gangan.To amma Israila ta ce ya yi wuri a iya zarginsu da aikata kisan.

Duniya ta yi tir da kisan yar jaridar mai shekaru 51, duk da tana sanye da rigar kariya daga harsashi, da kuma hular kwano da ke nuna alamun cewa yar jarida ce.

Da take magana da yan jarida a Geneva, Ravina Shamdasani ta ce Ofishin Kare Hakkin Bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya ya gano cewa ” harsashin da ya kashe Abu Aqla da wanda ya jikkata abokin aikinta Ali Sammoudi ya fito ne daga dakarun Israila”.

”Harsashi biyu aka harbo, inda daya ya jikkata Ali Sammoudi a kafada, yayin da daya ya shiga kan Abu Aqla ya kuma kashe ta nan take”, in ji ta.

Sai dai Israila ta ce tana kan gudanar da nata bincike kan kisan, kuma duk da ta gano cewa harsashin bindigar soja ne ya yi harbin, to amma tana bukatar a bata harsashin da ke hannun Falasdinu don ta kammala binciken.

To amma gwamnatin Falasdinu ta ce ba zata bada harsashin ba don bata amince da Isra’ila ba.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp