Gwamnatin shugaba Biden na Amurka ta ce, Isra’la na da damar kare kanta tare da mayar da martani kan harin da Iran ta kai mata a farkon watan da muke ciki.
To sai dai mista Biden ya faɗa wa Isra’ila cewa ba ya goyon bayan ta kai hari kan tashar makaman nukiliyar Iran, saboda fargabar hakan zai haifar da ƙaruwa da faɗaɗar yaƙin.
Haka kuma ya ce Amurka ba za ta goyi bayan kai wa rijiyoyin man Iran hare-hare ba.
“Idan da ni ne Isra’ila zan kai hari ne kan wasu abubuwan, amma ba rijiyoyin manta ba”, kamar yadda ya faɗa ranar 4 ga watan Oktoba.
Isra’ila ta ce hare-haren da ta kai wa Iran, ta kai su ne kan sansanonin sojinta.