Shugabannin ƙasashen Larabawa na neman goyon bayan ƙasashen duniya kan shirinsu na sake gina Gaza wanda zai bai wa mazauna yankin miliyan biyu damar ci gaba da zama a yankin.
Da yake jawabi a birnin Alƙahira, shugaban Masar Abdel Fattah al-Sisi ya ce, za a tattauna batun a wani babban taron ƙasashen musulmi da za a yi a Saudiyya ranar Juma’a.
Ya ce “Masar ta kuma yi aiki tare da ƴan’uwanmu Falasɗinwa wajen kafa kwamitin gudanarwa na kwararru masu zaman kansu, waɗanda za a bai wa amanar tafiyar da zirin Gaza bisa ƙwarewar mambobinsa.
Hamas dai ta yi maraba da ƙudurin kafa wannan kwamitin, amma Fadar White House da Isra’ila sun yi watsi da ƙudirin, suna masu cewa ba a yi la’akari da asalin yadda abubuwa suke a ƙasa a Gaza ba.