fidelitybank

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Date:

Isra’ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da shugaban Faransa Emmanuel Macron ke shirin ɗauka na amincewa da kafa ƙasar Falasdinawa a watan Satumba mai zuwa.

Faransa ita ce ƙasa ta farko cikin ƙasashen G7 – ƙasashe mafiya ƙarfin tattalin arziki a duniya – da za ta fito fili ta bayyana matsayinta na goyon bayan kafa ƙasar Falasdinawa.

Sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, ya bayyana a wani saƙo da ya wallafa a shafukan sada zumunta cewa wannan mataki na Macron yana da haɗari, yana mai cewa Hamas za ta yi amfani da shi wajen yaɗa farfaganda.

Haka zalika firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce wannan mataki tamkar ƙarfafa ayyukan ‘yan ta’adda ne.

Sai dai ƙasar Saudiyya ta yabawa shirin shugaban Faransa, tana mai cewa Macron ya kafa tarihi da wannan mataki.

Mahukuntan Falasdinu da ƙungiyar Hamas ma sun nuna gamsuwa tare da maraba da wannan yunkuri.

spw news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi – Thailand

Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...
X whatsapp