fidelitybank

ISAWP na raba tsofaffin kudade a tafkin Chadi

Date:

Gabanin cikar wa’adin babban bankin Najeriya, CBN, manufar ita kuwa kungiyar Islamic State of West Africa Province, ISWAP, an bayyana cewa mambobin kungiyar sun raba wasu makudan kudade na tsofaffin kudade ga matafiya a tafkin Chadi.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar a kan babbar hanyar Maiduguri/Monguno bayan kauyen Mairari da ke karamar hukumar Guzamala ta jihar Borno.

An ce ‘yan kungiyar ta ISWAP sun tuka manyan motocin bindiga guda biyu tare da sanye da katangar sojoji.

Wani mazaunin yankin mai suna Bakura Ibrahim ya ce maharan sun ajiye kansu a karkashin wata bishiya sannan suka tsaya a bakin titi dauke da jakunkunan tsofaffin kudin naira, inji rahoton Daily Trust.

“Mun bar Monguno da misalin karfe 12 na rana. Da muka tunkari Mairari, babu shingayen binciken ababen hawa a kewayen yankin, sai muka tsorata.

“Sun tambayi ko za mu je Maiduguri, daga nan ne suka fara bai wa kowane mutum N100,000 tsohon takardun kudi, amma ba mu yarda ba,” in ji shi.

Wata majiya ta kara da cewa kungiyar ta ce kawai su je bankuna su canza kudin zuwa sabbin takardun kudi, kuma “sun ce Allah Ya sa su amfane ku.”

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp