fidelitybank

Ireland, Sifaniya, Norway sun amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa a hukumance

Date:

Ƙasar Ireland ta zama ƙasa ta baya-bayan nan da ta amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa, inda ta bi sawun Sifaniya da Norway, waɗanda suka yi hakan a safiyar yau.

“Gwamnati ta amince da Falasɗinu a matsayin ƙasa mai ‘yanci da kuma cin gashin kanta, kuma mun yarda za mu ƙulla alaƙar difilomasiyya tsakanin Dublin da Ramallah,” a cewar wata sanarwa.

Za a tura jakadan Ireland zuwa Falasɗinu “tare da cikakken Ofishin Jakadancin Ireland a Ramallah,” in ji sanarwar.

Ita ma Norway ta yabi matakin da ta ɗauka a matsayin “rana ta musamman”, inda Ministan Harkokin Waje Espen Barth Eide ya ce ƙasarsa na cikin waɗanda suka fi goyon bayan kafa ƙasar Falasɗinawa sama da shekara 30″.

“Irin wannan rana da Norway ta amince da ƙasar Falasɗinawa a hukumance ta musamman ce a alaƙar ƙasashen,” a cewar Eide, yana mai cewa “abin takaici ne yadda gwamnatin Isra’ila ta gaza wajen nuna kyakkyawar niyya” wajen cimma ƙasa biyu.

Sifaniya kuwa ta amince da Falasɗinu ne bayan majalisar ministoci ta amince da hakan, in ji mai magana da yawun gwamnatin ƙasar.

Pilar Alegria ta ƙara da cewa majalisar “ta amince da mataki mai muhimmanci na amincewa da ƙasar Falasɗinu, wanda ke da manufa ɗaya tilo: don taimaka wa yunƙurin zaman lafiya tsakanin Falasɗinawa da Isra’ila”.

Firaministan Sifaniya Pedro Sanchez ya faɗa kafin ya gana da majalisar tasa cewa “amincewa da Falasɗinu a matsayin ƙasa ba abin tarihi ba ne kawai…sharaɗi ne na cimma zaman lafiya”.

Firaministan Ireland Simon Harris ya ce kafa ƙasa biyu ta Isra’ila da Falasɗinawa “ita ce hanya ɗaya da Isra’ila da Falasɗinawa za su rayu kafaɗa da kafaɗa cikin aminci”.

Da safiyar yau Talata ya ce akwai wani sabon salo “abin ƙyama kuma maras daɗin ji” inda Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya kwatanta kisan Falasɗinawa da “‘tsautsayi'”.

Harris na magana ne kan harin Isra’ila a sansanin gudun hijira da ya kashe aƙalla mutum 45 ranar Lahadi. In ji BBC.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp