Ɗaruruwan mutane sun hau kan titunan birnin Tehran na Iran ɗauke da take iri-iri na yin tir da Isra’ila.
Kazalika wasu da yawa sun riƙe tutocin ƙasar da kuma na Falasɗinawa.
Da yawan waɗanda suka taru sun kuma riƙe hotunan jagoran addini na ƙasar, Ayotollah Ali Khamenei.
Zanga-zangar na zuwa ne awanni bayan harin da Isra’ilar ta kai yankin Isfahan mai ɗumbin tarihi a matsayin ramuwa kan harin da Iran ta kai mata a makon da ya wuce.