fidelitybank

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan mutane uku

Date:

Hukumomi a Iran sun zartar da hukuncin kisa kan wasu mutane uku bisa alaƙa da zanga-zangar ƙin jinin gwamnati da aka gudanar a ƙasar a bara, kamar yadda ma`aikatar shari`a ta ƙasar ta bayyana.

An yanke wa mutanen uku hukuncin ne bisa zarginsu da hannu a harin da ya kashe jami`an tsaro uku a Isfahan, a watan Nuwamba.

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty international ta ce, an yi musu shari`a ba bisa ƙa`ida ba tare da zargin an azabtar da su.

An rataye wasu ƴan zanga-zangar huɗu tun watan Disamba.

An bayar da rahoton cewa an yanke wa wasu da dama hukuncin kisa ko kuma an tuhume su da aikata manyan laifuka.

Zanga-zangar dai ta mamaye duk faɗin jamhuriyar Musulunci ta Iran bayan mutuwar wata mata baƙurɗiya mai shekaru 22, Mahsa Amini, a hannun ƴan sanda bayan zargin ta da sanya hijabi ba daidai ba.

Mutanen uku da aka zartar wa hukunci a ranar juma`a- Majid Kazemi mai shekaru 30, da Saleh Mirhashemi mai shekaru 36, da kuma Saeed Yaqoubi mai shekaru 37- an kama su ne bayan zanga-zangar da aka yi a tsakiyar birnin Isfahan a ranar 16 ga watan Nuwamba, inda aka harbe wasu jami`an rundunar `yan sandan farin kaya ta Basij guda biyu tare da wani ɗan sanda.

Majiyoyi sun shaida ma ƙungiyar kare haƙƙin bil`adama cewa an tilasta wa mutanen amsa laifinsu ne, sannan aka azabtar da su tare da tilasta musu yin kalaman ɓatanci waɗanda suka zama tushen laifukan da ake tuhumarsu da su .

An yi zargin cewa masu yi musu tambayoyi sun ajiye Kazemi a kife, suka nuna masa faifan bidiyo na yadda suke azabtar da dan uwansa, inda suka yi masa kisan gilla tare da yi masa barazanar kashe sauran `yan uwansa.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp