fidelitybank

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Date:

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin kisa sakamakon kama su da laifin aikata fyaɗe, kamar yadda kamfanin labarai na Mizan mai alaƙa da ma’akatar shari’a ya ruwaito.

An aiwatar da hukuncin ne da tsakar daren da ya gabata a wani gidan yari da ke birnin Gorgan.

Heidar Asiabi, shugaban sashen shari’a na lardin, ya ce an fara bincike ne bayan wata mace ta shigar da ƙorafin yin garkuwa da ita.

Bayan tsananta bincike ne kuma wasu matan uku suka fito da zargin aikata fyaɗe. “Saboda girma da kuma kamanceceniya wajen aikata laifin aka kafa wata tawaga ta musamman da ta ƙunshi alƙalai da jami’an tsaro,” in ji Asiabi.

Bayan gano gungun mutum ukun cikin gaggawa, an kai su kotu tare da yanke musu hukunci, inda ita ma kotun ƙoli ta amince da shi.

Iran ta zartar wa aƙalla mutum 901 hukuncin kisa a 2024 kaɗai, a cewar Volker Turk, shugaban hukumar kare haƙƙi ta Majalisar Ɗinkin Duniya.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...
X whatsapp