fidelitybank

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Date:

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin kisa sakamakon kama su da laifin aikata fyaɗe, kamar yadda kamfanin labarai na Mizan mai alaƙa da ma’akatar shari’a ya ruwaito.

An aiwatar da hukuncin ne da tsakar daren da ya gabata a wani gidan yari da ke birnin Gorgan.

Heidar Asiabi, shugaban sashen shari’a na lardin, ya ce an fara bincike ne bayan wata mace ta shigar da ƙorafin yin garkuwa da ita.

Bayan tsananta bincike ne kuma wasu matan uku suka fito da zargin aikata fyaɗe. “Saboda girma da kuma kamanceceniya wajen aikata laifin aka kafa wata tawaga ta musamman da ta ƙunshi alƙalai da jami’an tsaro,” in ji Asiabi.

Bayan gano gungun mutum ukun cikin gaggawa, an kai su kotu tare da yanke musu hukunci, inda ita ma kotun ƙoli ta amince da shi.

Iran ta zartar wa aƙalla mutum 901 hukuncin kisa a 2024 kaɗai, a cewar Volker Turk, shugaban hukumar kare haƙƙi ta Majalisar Ɗinkin Duniya.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...
X whatsapp