Iran ta yi Allah wadai da harin Amurka da ta bayyana da na ”jahilci” kan jirgin dakon mai na ƴantawayen Houthi a tekun Yemen – da ya kashe fiye da mutum 74.
Ƙungiyar wadda ke samun goyon bayan Iran ta ce fiye da mutum 170 ne suka samu raunuka a sanadiyyar harin.
Hotunan da aka yaɗa a gidan talbijin mallakin ƙungiyar, sun nuna yadda ɓaraguzan jirgin ke ƙonewa, yayin da ma’aikatan agaji na ƙungiyar Red Cresent ke ciro gawarwaki daga wurin da lamarin ya faru.
Rundunar sojin Amurka sun ce manufar harin – da aka kai a Tekun Ras Isa – shi ne taƙaita kai wa ƙungiyar kayan aiki da kuɗaɗe.
A watan da ya gabata ne sojojin Amurka suka tsananta hare-hare kan ƴantawayen Houthi.