Iran ta ce ta zartar da hukuncin kisa kan wasu mutum huɗu waɗanda ta zarga da aikin leken asiri ga ƙasar Isra’ila.
Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ce an aiwatar da hukuncin kisan da safiyar yau Lahadi.
A watan Mayu, dakarun juyin juya hali na ƙasar suka ce sun kama wasu mutane da suka zarga da sata da garkuwa da mutane da kuma kwace.
Ƙasashen Isra’ila da Iran sun kasance maƙiyan juna, inda Iran ɗin ke goyon bayan ƙungiyoyin da ke adawa da Isra’ila irin su Hezbollah da Hamas.