Iran ta aiwatar kisa kan mutum na biyu a bayyanar jama’a da aka kama da hannu a zanga-zangar kin jinin gwamnati da aka shafe watanni biyu ana yi.
Ma’aikatar shari’ar kasar ta ce, an rataye mutumin mai suna Majid Reza Rahnavard, a birnin Mashhad.
An same shi da laifin caka wa wasu jami’an tsaro biyu wuka abin da ya yi sanadiyyar rasa rayukansu.
A ranar Alhamis din data wuce ne aka kashe mutum na farko da aka kama da irin wannan laifin.
An kashe Majid Reza ne kwanaki 23 bayan an kama shi.
Wannan mataki na mahukuntan kasar na shan suka daga kasashen yamma.