fidelitybank

Iran ta nuna irin karfin da take da shi a lokacin da ta kai wa Isra’ila hari – Khamenei

Date:

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ali Ayatullah Khamenei ya ce, kasarsa ta nuna irin karfin da take da shi a lokacin harin da aka kai wa Isra’ila, ba tare da la’akari da adadin da aka kai mata hari ba.

Makwanni biyu da suka gabata Iran ta harba jiragen yaki marasa matuka da makamai masu linzami kan Isra’ila a matsayin ramuwar gayya kan harin da aka kai ofishin jakadancinta a Damascus na kasar Siriya a ranar 1 ga Afrilu.

Amma yawancin jirage marasa matuka da makamai masu linzami tsarin tsaron Isra’ila ne ya kame su.

Duk da haka, Khamenei ya yabawa Sojojin Iran da suka kai wa Isra’ila hari.

Da yake magana a ranar Lahadin da ta gabata, ya ce: “Nawa ne makami mai linzami da aka harba, kuma nawa ne aka harba musu, ba ita ce tambaya ta farko ba, abin da ke da muhimmanci shi ne Iran ta nuna karfinta a yayin wannan farmakin.

Khamenei ya kara da cewa, “A cikin farmakin na baya-bayan nan, sojojin sun yi nasarar rage tsadar kayayyaki tare da kara samun nasarori,” in ji Khamenei, yana mai kira ga jami’an soji da su ci gaba da bin sabbin hanyoyin soja tare da koyan dabarun abokan gaba.

Amma, da sanyin safiyar Juma’a, wasu fashe-fashe sun mamaye birnin Isfahan na kasar Iran, lamarin da da dama suka yi imanin cewa harin ramuwar gayya ne daga Isra’ila.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taÉ“a barin Iran ta Æ™era makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaÆ™i – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama É—an kasar China da zargin kai wa Æ´an Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp