fidelitybank

Iran ta nemi Saudiyya ta saki ɗan ƙasar ta da ta kama a aikin Hajji

Date:

Kasar Iran ta yi kira ga Saudiyya da ta saki daya daga cikin ƴan kasarta da aka kama a lokacin aikin Hajji, yayin da kasashen biyu da ke takaddama da juna suka soma dinƙe ɓarakar da ke tsakaninsu.

A wata sanarwa Jamhuriyar ta Musulunci ta bayyana cewa an tsare dan ƙasarta dangane da wata wayar tarho tsakanin ministan harkokin waje Hossein Amir-Abdollahian da takwaransa na Iraq Fuad Hussein.

Iraki ta cigaba da shiga tsakani domin sulhunta Saudiyya da Iran tun watan Afrilun shekarar da ta gabata.

“A wayar, ministan harkokin wajen Iran ya yi bin sawu kan makomar dan Iran da aka tsare a Saudiyya lokacin aikin Hajji kuma ya yi ba da saƙon kira a sako shi,” a cewar sanarwar.

Sanarwar ba ta ba da ƙarin bayani a kan sunan wanda aka tsare ko dalilin tsare shi a lokacin aikin Hajji da aka yi a watan da ya gabata ba. Kimanin mutane 780,000 ne suka yi aikin Hajjin wannan shekara kamar yadda jami’an Saudiyya suka bayyana. In ji BBC.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp