Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da inganta sinadarin Uranium, mako guda bayan da Amurka ta haɗa hannu da Isra’ila wajen kai harin bama-bamai a manyan cibiyoyin nukiliyarta.
Mataimakin ministan harkokin wajen ƙasar Majid Takht-Ravanchi ya shaida wa BBC cewa za a iya tattauna iya matakin da za a iya kai wa na sarrafa sinadarin.
Ya ce “muna tsakiyar tattaunawa sai kwatsam aka afka mana da hare-hare kuma duk waɗanda ke sukar mu ya kamata su soki irin halin rashin mutuncin da aka nuna mana.”
Mataimakin ministan ya shaida wa wakiliyar BBC da ke ziyara a Tehran cewa gwamnatin ƙasarsa ba za ta shiga wata tattaunawa kan nukiliya ba, sai idan gwamnatin Trump ta ba da tabbacin ba za ta kai mata hari ba yayin da tattaunawar ke gudana.