Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra’ila yayin da Iran ke ci gaba da mayar da martani kan hare-haren da ake kai mata.
An ji ƙarar fashewar abubuwa a biranen Isra’ila da suka haɗa da birnin Kudus da kuma Tel Aviv.
Wani ɗan jarida kuma mazaunin birnin Tel Aviv, Gideon Levy, ya shaida wa BBC an kakkabo wasu makaman linzami wasu kuma sun faɗi ƙasa.
Akwai aƙalla guda biyu da suka faɗi kai-tsaye kan gine-gine inda suka ruguza wasu ɓangarorinsu.
Kafofin yaɗa labaran Isra’ila sun ce mutane uku ne suka mutu, yayin da wasu da dama suka jikkata tun bayan da Iran ta fara kai hare-haren.