Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra’ila inda ta kai hare-hare a yankin arewaci da kuma tsakiyar ƙasar.
Aƙalla mutum takwas ne aka tabbatar sun mutu, inda hukumomi suka ce wasu 200 sun jikkata.
An kashe wasu mata a wata unguwar Larabawa da ke gabashin birnin Haifa.
An kuma kai hari kan wani gini a garin Bat Yam da ke tsakiyar ƙasar, inda wasu ‘yan Isra’ila uku suka mutu.
Wakilin BBC ya ce hotuna da aka ɗauka a yankin Bat Yam da ke kudancin birnin Tel Aviv – sun nuna ɓarnar da hare-haren suka yi.
An kuma ji ƙarar abubuwa masu fashewa a birnin Kudus.
Tun da farko sojojin Isra’ila sun kai hare-hare ta sama kan birnin Tehran, suna masu cewa sun kai hari kan gine-gine masu alaƙa da shirin nukiliyar Iran.