Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta fara abin da ta kira martani mafi girma da nasara kan hare-haren Amurka a cikin ƙasar.
Kamfanin dillancin labaran ƙasar na Tasnim ya ce dakarun juyin juya halin ƙasar sun ƙaddamar da hare-haren makamai masu linzami kan sansanin sojin Amurka da ke Qatar da Iraƙi
A ƴan mintunan da suka wuce ne aka samu labaran jin ƙarar abubuwan fashewar a Qatar.