Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta bayyana cewa, an tsawaita dakatar da duk wasu tashi da saukar jiragen sama har zuwa ƙarfe 02:00 na safe agogon ƙasar a ranar Talata wato ƙarfe 11:30 na dare agogon BST na Litinin, kamar yadda kafafen yaɗa labaran gwamnati suka ruwaito.
Tun makon da ya gabata ne Iran ta rufe sararin samaniyarta ga dukkan jiragen kasuwanci saboda tashe-tashen hankula da ake fama da su.
Rundunar sojin Isra’ila ta ce ta kankane sararin samaniyar birnin Tehran na Iran, inda jiragen yaƙin Isra’ila ke amfani da shi wajen kai farmaki kan wasu muhimman wurare a cikin ƙasar.