Sabon shugaban Iran, Masoud Pezeishkian, ya gabatar da jawabin farko a taron MDD na shekara-shekara wanda yake haɗa shugabanni duniya a birnin Newyork.
Mista Pezeishkian ya yi amfani da damar wajen caccakar Isra’ila da zarginta da rura wutar fittina a Gabas ta Tsakiya da kuma Allah wadai da abin da ya bayyana da aikata laifukan take haƙƙin bil Adama a Gaza da aiwatar da ayyukan ta’addanci a Lebanon.
Duk da sake sukurkucewar alaƙa tsakanin ƙasarsa da manyan ƙasashe, Mista Pezeishkian ya bayyana cewa a shirye suke su kawo ƙarshen gumurzu da ƙasashen yammaci ke yi da su kan shirinsu na Nukilliya – sannan ya jadadda cewa gwamnatinsa ba ta da niyyar gaba ko rikici da kowacce ƙasa.
Shugaban hukumar kula da harokin Nukilliya a MDD, ya ce yana fatan zuwa Teheran a farkon watan Oktoba domin tattaunawa kan shirin nukilliyar Iran.