Iran ta zartar da hukuncin kisa na farko a kan ɗaya daga cikin masu zanga-zangar adawa da gwamnati, wadda ta zamo ƙarfen-ƙafa ga hukumomin ƙasar tun cikin watan Satumba.
An kama Mohsen Shekari da laifin raunata jami’in tsaro na sa-kai da kuma datse hanya a babban birnin ƙasar, Tehran.
Saboda haka ne aka gurfanar da shi bisa zargin yin fito-na-fito da dokokin Allah, wanda hukuncinsa shi ne kisa.
An kai Mr Shekari wani wurin da aka tsare shi kwana biyu gabanin rataye shi.
Aƙalla mutum 11 ne aka yanke wa hukuncin kisa tun bayan zanga-zangar da ta ɓarke a ƙasar sanadiyyar mutuwar wata matashiya mai suna Mahsa Amini.
Akwai wasu mutum 20 da ke cikin haɗarin fuskantar hukuncin kisa a ƙasar yanzu haka.