fidelitybank

Iran da ƙawayenta ba su jin tsoron yin fito na fito da Isra’ila – Ayatollah

Date:

Shugaban addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce, Iran da ƙawayenta ba su jin tsoron yin fito na fito da Isra’ila, duk da kashe shugabannin Hamas da Hizbollah da Isra’ilar ta yi.

Ayatollah Khamenei ya bayyana hakan ne a yayin da yake gabatar da hudubar Juma’a a babban massalacin Tehran, inda ya ce harin da Iran din ta kai wa Isra’ila halastacce ne kuma ɗan ƙaramin hukunci ne na laifukan da Isra’ilar take aikatawa.

Ya ce, “me ya kamata mu yi ? daga ɓangaren ƴan siyasa da dakarun soji da kuma sauran hukumomi, duk za mu hadu mu dauki matakin da ya dace, a lokacin da ya dace kamar dai yadda muka saba yi a baya.”

Shugaban addinin ya kuma yi wa shugaban Hizbollah da aka kashe Hassan Nasrullah addu’a tare da jinjina masa.

Ministan harakokin wajen Abbas Araghchi ya isa Lebanon domin ganawa da shugaban siyasar ƙasar.

Wannan ne karon farko da jagoran addunin na Iran ya yi huɗubar Juma’a, tun bayan kisan da Amurka ta yi wa kwamandan dakarun juyin juya hali Qassem Soleimani a Janairun 2020.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp