fidelitybank

Iran da ƙawayenta ba su jin tsoron yin fito na fito da Isra’ila – Ayatollah

Date:

Shugaban addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce, Iran da ƙawayenta ba su jin tsoron yin fito na fito da Isra’ila, duk da kashe shugabannin Hamas da Hizbollah da Isra’ilar ta yi.

Ayatollah Khamenei ya bayyana hakan ne a yayin da yake gabatar da hudubar Juma’a a babban massalacin Tehran, inda ya ce harin da Iran din ta kai wa Isra’ila halastacce ne kuma ɗan ƙaramin hukunci ne na laifukan da Isra’ilar take aikatawa.

Ya ce, “me ya kamata mu yi ? daga ɓangaren ƴan siyasa da dakarun soji da kuma sauran hukumomi, duk za mu hadu mu dauki matakin da ya dace, a lokacin da ya dace kamar dai yadda muka saba yi a baya.”

Shugaban addinin ya kuma yi wa shugaban Hizbollah da aka kashe Hassan Nasrullah addu’a tare da jinjina masa.

Ministan harakokin wajen Abbas Araghchi ya isa Lebanon domin ganawa da shugaban siyasar ƙasar.

Wannan ne karon farko da jagoran addunin na Iran ya yi huɗubar Juma’a, tun bayan kisan da Amurka ta yi wa kwamandan dakarun juyin juya hali Qassem Soleimani a Janairun 2020.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp