fidelitybank

Iran ce ta yi wa Trump kutse – Kwamitin yaƙin zaɓe

Date:

Kwamitin yaƙin neman zaɓen tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce an yi masa kutse a cikin bayanansa na cikin gida, kuma ya nuna alamun jami’an Iran ne ke yin hakan.

Shafin jaridar intanet ta Politico da ke Amurka, a jiya Asabar ya bayar da rahoton cewa an aika masa wasu takardun yaƙin neman zaɓe ciki har da takardun bincike na cikin gida da kwamitin yaƙin neman zaɓen na Trump ya yi a kan mataimakin Trump ɗin a zaɓen da za a yi, Sanatan Ohio, JD Vance.

Wani mai magana da yawun kwamitin yaƙin neman zaɓen ya gaya wa BBC cewa :“An samu waɗannan takardu ne ta haramtacciyar hanya daga wasu kafofi na ƙasar waje, da ke gaba da Amurka, da nufin katsa-landan a zaɓen 2024.”

Jaridar Politico ta ce ta tabbatar da sahihancin takardun. Sai dai kuma BBC ba ta tabbatar da sahihancin iƙirarin ba.

Sai dai kwamitin yaƙin neman zaɓen bai bayar da cikakken bayani ko wata sheda da ke tabbatar da takardun da aka yi satar fitar da su ba ga masu kutse na Iran ko kuma gwamnatin Iran.

Ko a lokacin zaɓen shugaban Amurka na 2020 kamfanin Microsoft ya fitar da irin wannan rahoton, da cewa masu kutse na Iran na harin yaƙin neman zaɓe na shugaban ƙasa.

Kamfanin ya ma ƙara da cewa masu kutsen na Iran sun yi haka a kai-a kai aƙalla a zaɓe uku na shugaban ƙasa a Amurka.

Haka su ma jami’an tsaron Amurka sun yi gargaɗin cewa Iran na shirin hallaka Donald Trump, to amma wannan ba shi da alaka da harin da aka kai masa a watan da ya wuce a Pennsylvania.

Kuma a ranar Talata ma’aikatar shari’a ta Amurka ta tuhumi wani ɗan Pakistan da ake zargi yana da alaƙa da Iran da shirin kashe jami’an Amurka, wanda a iya cewa har ma da shugaban ƙasar.

BBC ta tuntuɓi jami’an Iran domin jin ta bakinsu.

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp