fidelitybank

Iran ce ta yi wa Trump kutse – Kwamitin yaƙin zaɓe

Date:

Kwamitin yaƙin neman zaɓen tsohon shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce an yi masa kutse a cikin bayanansa na cikin gida, kuma ya nuna alamun jami’an Iran ne ke yin hakan.

Shafin jaridar intanet ta Politico da ke Amurka, a jiya Asabar ya bayar da rahoton cewa an aika masa wasu takardun yaƙin neman zaɓe ciki har da takardun bincike na cikin gida da kwamitin yaƙin neman zaɓen na Trump ya yi a kan mataimakin Trump ɗin a zaɓen da za a yi, Sanatan Ohio, JD Vance.

Wani mai magana da yawun kwamitin yaƙin neman zaɓen ya gaya wa BBC cewa :“An samu waɗannan takardu ne ta haramtacciyar hanya daga wasu kafofi na ƙasar waje, da ke gaba da Amurka, da nufin katsa-landan a zaɓen 2024.”

Jaridar Politico ta ce ta tabbatar da sahihancin takardun. Sai dai kuma BBC ba ta tabbatar da sahihancin iƙirarin ba.

Sai dai kwamitin yaƙin neman zaɓen bai bayar da cikakken bayani ko wata sheda da ke tabbatar da takardun da aka yi satar fitar da su ba ga masu kutse na Iran ko kuma gwamnatin Iran.

Ko a lokacin zaɓen shugaban Amurka na 2020 kamfanin Microsoft ya fitar da irin wannan rahoton, da cewa masu kutse na Iran na harin yaƙin neman zaɓe na shugaban ƙasa.

Kamfanin ya ma ƙara da cewa masu kutsen na Iran sun yi haka a kai-a kai aƙalla a zaɓe uku na shugaban ƙasa a Amurka.

Haka su ma jami’an tsaron Amurka sun yi gargaɗin cewa Iran na shirin hallaka Donald Trump, to amma wannan ba shi da alaka da harin da aka kai masa a watan da ya wuce a Pennsylvania.

Kuma a ranar Talata ma’aikatar shari’a ta Amurka ta tuhumi wani ɗan Pakistan da ake zargi yana da alaƙa da Iran da shirin kashe jami’an Amurka, wanda a iya cewa har ma da shugaban ƙasar.

BBC ta tuntuɓi jami’an Iran domin jin ta bakinsu.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp