Iraƙi ta kira jekadanta a Sweden domin adawa da zargin ƙona Al Kur’ani mai tsarki a ƙasar.
Sanarwar daga ma’aikatar harakokin waje da kafar Shafaq ta wallafa a ranar Lahadi, gwamnatin Iraƙi ta ce kona Al Kur’ani abu ne mai tsanani kan alaƙar Sweden da al’ummar Musulmi baki ɗaya, musulmi a ƙasashen larabawa da Musulmin Turai.
An shafe kwana uku ana zanga-zanga a Sweden kan adawa da masu tsauttsauran ra’ayi da ke ƙyamar baƙi da suka kona Al Kur’ani tare da barazanar ci gaba da ƙonewa.
Zanga-zangar ta ɓarke a Malmo a ranar Asabar bayan gangamin shugaban jam’iyyar masu kyamar Musulmi Rasmus Paludan.
An ƙone motoci kuma masu znaga-zanga sun ta jifar ƴan sanda da duwatsu.