fidelitybank

IPOB ‘yan ta’adda ne – Birtaniya

Date:

Gwamnatin Birtaniya ta bi sahun ta Najeriya wajen ayyana ƙungiyar ‘yan aware masu neman kafa ƙasar Biafra a kudancin Najeriyar a matsayin ta ‘yan ta’adda.

Hakan na nufin Birtaniya ba za ta bai wa mambobin ƙungiyar mafaka ba kamar yadda ta yi niyya a baya. A cewar BBC.

Tun a 2017 ne gwamnatin Najeriya ta ayyana IPOB a matsayin ta ‘yan ta’adda saboda kashe-kashen da hukumomi ke zargin ta da aikatawa a jihohin kudu maso gabashin ƙasar da suka haɗa da Anambra, da Abia, da Ebonyi, da Imo, da Enugu.

Matakin na ƙunshe ne cikin kundin ayyukan hukumar harkokin cikin gida ta Birtaniya, inda ta ce ƙungiyar “yan ta’adda ce sakamakon ayyukan tashin hankali da take aikatawa”.

Lamarin na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan gwamnatin Najeriya ta ce IPOB ce ta kashe wasu sojojinta biyu mace da namiji da ke shirin yin aure a Jihar Imo da ke yankin na kudu maso gabas. Sai dai ƙungiyar ta musanta zargin.

Gwamnatin Najeriya ta gurfanar da Nnamdi Kanu shugaban ƙungiyar, wanda ke da shaidar zama ɗan ƙasar Birtaniya a gaban kotu, tana mai zargin sa da haddasa tashin hankali da raba kan ‘yan ƙasa.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Wa’adin da Najeriya ta bai wa Facebook na biyan tarar dala miliyan 290 ya cika

A ranar Litinin ne wa'adin da wata kotu ta...

Jami’an sa-kan Zamfara sun kashe Kacalla Ɗanbokolo ubangidan Turji

Gwamnatin jihar Zamfara da ke arewa maso yammcin Najeriya...

PDP ta gudanar da taron ta na kasa

Shugabani da gwamnonin da sauran masu ruwa da tsaki...

An ɗage jana’izar Aminu Ɗantata zuwa Talata

Gwamnatin Najeriya ta sanar da ɗage jana'izar fitaccen ɗankasuwar...

‘Yansanda sun kwace iko da sakatariyar PDP a Abuja

A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan...

Iran ta na da ‘yancin yin Nukiliyar ta – Ravanchi

Iran ta dage kan hakkinta na ci gaba da...

Tawagar Gwamnatin Kano ta shilla Saudiyya zuwa jana’izar Dantata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci...

Tawagar Jami’an gwamnati da Malamai sun tafi jana’izar Dantata

Wata tawaga daga gwamnatin Tarayya, ta isa ƙasar Saudiyya...

Taimakon da Dantata ya ke yi wa Al’umma tarihi ba zai manta da shi ba – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bayyana alhininsa...

Gwamnan Kano ya sauya wa hukumar Wasanni suna

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya sauya wa...

Dalilin da ya sa Wake ya karye a Najeriya – Ƙungiyar Manoma

Ƙungiyar manoman wake a kasar nan, ta bayyana amfani...

Masu shan Taba Sigari sun shiga rudani a Faransa da firgici

A yau ne sabbin dokokin hana shan taba a...
X whatsapp