Gwamnatin Birtaniya ta bi sahun ta Najeriya wajen ayyana ƙungiyar ‘yan aware masu neman kafa ƙasar Biafra a kudancin Najeriyar a matsayin ta ‘yan ta’adda.
Hakan na nufin Birtaniya ba za ta bai wa mambobin ƙungiyar mafaka ba kamar yadda ta yi niyya a baya. A cewar BBC.
Tun a 2017 ne gwamnatin Najeriya ta ayyana IPOB a matsayin ta ‘yan ta’adda saboda kashe-kashen da hukumomi ke zargin ta da aikatawa a jihohin kudu maso gabashin ƙasar da suka haɗa da Anambra, da Abia, da Ebonyi, da Imo, da Enugu.
Matakin na ƙunshe ne cikin kundin ayyukan hukumar harkokin cikin gida ta Birtaniya, inda ta ce ƙungiyar “yan ta’adda ce sakamakon ayyukan tashin hankali da take aikatawa”.
Lamarin na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan gwamnatin Najeriya ta ce IPOB ce ta kashe wasu sojojinta biyu mace da namiji da ke shirin yin aure a Jihar Imo da ke yankin na kudu maso gabas. Sai dai ƙungiyar ta musanta zargin.
Gwamnatin Najeriya ta gurfanar da Nnamdi Kanu shugaban ƙungiyar, wanda ke da shaidar zama ɗan ƙasar Birtaniya a gaban kotu, tana mai zargin sa da haddasa tashin hankali da raba kan ‘yan ƙasa.