Kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, a ranar Lahadin da ta gabata ta yi zargin cewa sashen leken asirinta, ta bankado wani shiri na kashe dan takarar shugaban kasa na jamâiyyar PDP, Atiku Abubakar, a yankin Kudu maso Gabas.
Emma Powerful, mai magana da yawun kungiyar IPOB ya yi zargin cewa kisan Atiku za a dora wa mabiyan Peter Obi da Labour Party, LP.
Sanarwar ta ce: âBisa laâakari da matsalar rashin tsaro da gwamnati ta addabi Najeriya, mu da masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) da kuma iyalan masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB) a karkashin jagorancin babban mai fafutukar âyanto Mazi Nnamdi Okwuchukwu Kanu muna fatan sanar da jamaâa. akan rahoton sirri da muka samu na shirin kai wa Alhaji Atiku Abubakar hari a yankin Kudu maso Gabas da dora alhakinsa akan IPOB, ESN ko dan takarar shugaban kasa, magoya bayan Peter Obi, kungiyar Obidient.
Karanta Wannan:Â ‘Yan Najeriya za ku ci gajiyar sauya kudi na CBN – Peter Obi
âSashin leken asirin IPOB, M-Branch ya bankado wani shiri da wasu marasa kishin siyasa ke yi na haifar da rikici a kasar nan kan IPOB da Ndigbo a duk fadin kasar nan.
âWannan kungiya na shirin kashe Atiku Abubakar a yankin Kudu maso Gabashin Najeriya kuma ta ce wasu âyan bindiga da ba a san ko su waye ba, ESN/IPOB, ko kuma kungiyar Obidient ne suka aikata ta.â In ji Daily Post.