Mazauna yankin Kudu maso Gabas a Najeriya sun kasance a gidajensu a yau Laraba yayin da ake ci gaba da shari’ar jagoran ƙungiyar neman ɓallewa daga ƙasar ta Indigenous People of Biafra (IPOB) Nnamdi Kanu.
A yau Laraba ne kotu ke ci gaba da shari’ar Nnamdi Kanu kan tuhumar da gwamnatin Najeriya ke yi masa game da cin amanar ƙasa da tayar da hankali da cin mutuncin Shugaba Buhari.
Tun farko ƙungiyar ta ayyana kowace Litinin a matsayin ranar zama a gida har sai an sako shugaban nasu, sai dai ta ce ta janye dokar. Amma duk da haka mazauna jihohin yankin ba sa iya fita harkokinsu saboda fargaba. In ji BBC.
Mazauna garin Enugu babban birnin Jihar Enugu ba su fita harkokinsu ba a yau Laraba.
Haka lamarin yake a Jihar Ebonyi, inda wurare irinsu Magamar Vanco da Gunning da Shataletalen Abacha suka kasance fayau.