Kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB, ta bayyana Mazi Chika Edoziem a matsayin sabon shugabanta.
IPOB ta ce Edoziem zai gudanar da ayyukanta har sai an sako shugabanta Nnamdi Kanu.
Wata sanarwa da mai magana da yawun kungiyar, Emma Powerful, ya fitar ta ce Edoziem zai bar aikin shugabancin ga Kanu idan aka sake shi.
Sanarwar ta kara da cewa: “Domin kaucewa shakku, ‘yan asalin yankin Biafra (DOS), karkashin jagorancin Mazi Chika Edoziem, ita ce ke jagorantar al’amuran Biafra; duk lokacin da shugabanmu Mazi Nnamdi KANU ya fito, sai ya mayar masa da tsarin kungiyar IPOB.”
Ana kyautata zaton Edoziem shine mataimakin shugaban kungiyar IPOB.
Yanzu haka dai Kanu na tsare a hannun jami’an tsaro na farin kaya, DSS.
Hukumar DSS dai ta rike shugaban na IPOB ne tun bayan da aka sake kama shi tare da mayar da shi gida daga Kenya a shekarar 2011.