fidelitybank

IPOB sun kashe mace da ƴaƴanta 4 – Sarkin Hausawa

Date:

Kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra (IPOB), Eastern Security Network (ESN) anyi yi zargin sun kashe wata mata da ‘ya’yanta hudu da wasu shida a jihar Anambra.

Matar mai juna biyu da ‘ya’yanta da aka kashe a Isulo, karamar hukumar Orumba ta Arewa, sun fito ne daga yankin Arewacin kasar nan.

Kashe-kashen ya nuna wani sabon koma baya a hare-haren da ‘yan ta’addar IPOB ke kaiwa wadanda ba ‘yan asalin kasar ba, wadanda kuma suke kai hari kan alamar hukuma da suka hada da ‘yan sanda da sojoji.

Kisan ’yan Arewa da ake zargin kungiyar da ke fafutukar kafa kasar Biafra ce, ta yi shi ne kwanaki kadan bayan gano shugaban wani dan majalisar dokokin jihar Anambra, Okey Okoye da ‘yan ta’addan suka yi garkuwa da shi.

Sarkin Hausawa na karamar hukumar Orunba ta Arewa, Alhaji Sa’id Muhammad a ranar Litinin din da ta gabata ya bayyana cewa, ‘yan Arewa mazauna jihar Anambra sun kuduri aniyar barin jihar, saboda kashe-kashen da ‘yan ESN, reshen ‘yan banga da makami ke yi a kullum.

Muhammad wanda ya bayyana yadda lamarin ya faru ya shaida wa Aminiya cewa, kisan da wasu ‘yan bindiga suka yi wa matar mai ciki tare da ‘ya’yanta hudu ba sabon abu ba ne a gare su, domin an kashe mutanensa da yawa ta hanyar rashin kunya.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Anambra, Echeng E. Echeng a ranar Litinin din da ta gabata ya zargi al’ummar jihar da yin garkuwa da masu aikata laifuka a tsakaninsu.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp