fidelitybank

IPOB sun ƙara kai hari ofishin ƴan sanda a Imo

Date:

Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan kungiyar masu fafutukar kafa kasar Biafra/Eastern Security Network ne suka kai hari a shelkwatar ‘yan sandan yankin Obowo da ke Imo a ranar Litinin.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Imo, CSP Michael Abattam, ya bayyana haka a garin Owerri, inda ya ce, maharan sun tunkari ofishin ne daga wani daji.

Ya kara da cewa, sun jefa bama-baman fetur da na’urori masu fashewa wadanda suka fada sansanin ‘yan gudun hijira da ke bayan tashar da kuma kan wata motar da ta tsaya.

“Jami’an ‘yan sanda da wasu daga cikin ’yan sandan rundunar ne suka mayar da martani ga ‘yan ta’addan harbin bindiga da ya hana su shiga ofishin.

“A cikin haka, sun tilasta wa ‘yan bindigar komawa cikin dajin tare da raunuka daban-daban na harsashi.

“Jami’an ‘yan sandan sun yi musu zafafan fatattakar su, kuma a lokacin da suke tseguntawa daji, an gano bama-bamai uku da ba a tashe su ba, harsashi AK47 da aka kashe guda hudu da kuma harsashi masu rai guda biyar.

Ya kuma bayyana cewa an yi wa wani dan sandan da ya samu ‘yar rauni.

Kakakin ‘yan sandan ya kara da cewa, mukaddashin kwamishinan ‘yan sandan DCP Maman Giwa, wanda ya ziyarci wurin, ya yabawa jami’an tsaro da mutanen da suka dakile harin. A rahoton Daily Nigerian.

naija legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp