Gwamna Dave Umahi na jihar Ebonyi, ya ce, bai kamata a karbi masu fafutukar kafa kasar Biafra, IPOB ba a yankin Kudu maso Gabas, saboda munanan ayyukan da suke yi.
Gwamnan wanda kuma ke neman tikitin takarar shugaban kasa na jamâiyyar APC, ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar bakuncin shugabanni da mambobin kungiyar Editocin Najeriya a Abakaliki a karshen mako.
A cewar Umahi, tashin hankalin da kungiyar âyan awaren ke yi ba zai haifar da ‘da mai ido ba a yankin, inda ya nuna cewa ya yi wannan kira ne tun yana dan jamâiyyar PDP.
Ya bayyana cewa IPOB ta yi nasarar yaudarar âyan kabilar Igbo cewa, yankin siyasar yankin yana kutsawa da baki, inda ya yi zargin cewa suma suna yin kalaman nuna kiyayya.
Umahi ya ce, âAkwai siyasa ta wuce gona da iri a wannan yanki, kuma dole ne a daina, tun da muka fara musamman kafin na koma na, muna aiki tare kuma ina fafutikar ganin IPOB ba ta mana dadi saboda tada zaune tsaye da ake yi. haduwa ba daidai ba.