Shugaban kungiyar kwallon kafa ta Lobi Stars (FC), Engr Benson Abounu, ya bayyana cewa, gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom ya bayyana kwarin guiwar sabbin shugabannin kungiyar na fitar da Lobi daga matakin faduwa.
Abounu, wanda mataimakin gwamnan jihar ne ya bayyana hakan a lokacin da ya karbi bakuncin sabon kocin kuma aka gabatar da sabon kocin, Baba Ganaru a ofishinsa a ranar Juma’a.
Idan dai ba a manta ba, a farkon makon ne aka nada Dominic Iorfa a matsayin sabon mataimakin shugaban kungiyar Lobi Stars, wanda aka bi sawun Ganaru a matsayin babban koci a ranar Alhamis.
Abounu ya yi alkawarin cewa Gwamna Ortom ya tabbatar masa da cewa zai baiwa kungiyar goyon bayansa.
A cewarsa, “Shi (Ortom) ya bayyana amincewa da mutumin Dominic Iorfa da kuma ikonsa na fitar da kungiyar daga faduwa.