fidelitybank

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: An yi wa Dan shekara 7 yankan Rago a Kano

Date:

Wasu ɓata gari da ba a san ko su waye ba, sun yi wa wani ƙaramin yaro Junaidu Ibrahim dan shekaru 7 yankan Rago a garin Zangon Dan Abdu da ke Karamar Hukumar Rimingado a Kano.

Mahaifin yaron Ibrahim Aliyu ya shaida wa Arewa Updates cewa, a ranar Lahadi yana zaune aka zo aka sanar da shi an ga yaronsa an fasa masa kai a gona, amma da ya je sai ya tarar an yi masa yankan rago ne.

Shi ma mai unguwar yankin Ibrahim Chiroma ya ce, sun binciki yaron ba a cire komai na jikinsa ba, amma suna zargin ɓata garin jininsa suka tatsa.

A wani mai kama da wannan, ranar Asabar wasu ɓata gari sun rataye wata yarinya Fatima Sule ƴar shekaru 13 a jikin taga a unguwar Dandishe Yamma layin Malam Kamalu da ke Karamar Hukumar Dala a Kanon.

Rahotonnin da Arewa Updates ta samu sun nuna cewa lamarin ya faru ne a lokacin da mahaifiyar yarinyar ta tafi unguwa, amma da dawowarta ta tarar da ita rataye a mace.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Jami’in mu bai saci naira biliyan 6.5 ba – Gwamnatin Kano

Gwamnatin Jihar Kano ta karyata rahoton da ya zargi...

Gwamnatin Kano ta gargadi Matasa da ‘yan Gwangwan kan sayen kayan gwamnati

Gwamnatin Jihar Kano ta gargadi matasa da ’yan kasuwa...

NIMET ta gargai Borno kan ambaliya da sauran jihohi

A baya-bayan nan ne hukumar hasashen yanayi ta Najeriya...

An kashe kwamandan Boko Haram a tafkin Chadi

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun sanar da kisan wani jagoran...

Hisbah za ta yi wa ‘yan Daban Kano aure

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta sanar da wani...

Ganduje ya dawo Najeriya bayan ya shafe wata guda a Landan

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa, Dr. Abdullahi Ganduje,...

Barrister Sa’idu ya kama aiki bayan ya maye gurbin Muhyi Magaji

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya rantsar...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

An ceto Mutane 26 da kwale-kwale ya kife da su a Sokoto

An samu nasarar ceto mutum 29 bayan hatsarin kwale-kwale...

Barau zai mayar da filin wasan BUK na zamani

Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, ya...
X whatsapp