fidelitybank

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: An yi wa Dan shekara 7 yankan Rago a Kano

Date:

Wasu ɓata gari da ba a san ko su waye ba, sun yi wa wani ƙaramin yaro Junaidu Ibrahim dan shekaru 7 yankan Rago a garin Zangon Dan Abdu da ke Karamar Hukumar Rimingado a Kano.

Mahaifin yaron Ibrahim Aliyu ya shaida wa Arewa Updates cewa, a ranar Lahadi yana zaune aka zo aka sanar da shi an ga yaronsa an fasa masa kai a gona, amma da ya je sai ya tarar an yi masa yankan rago ne.

Shi ma mai unguwar yankin Ibrahim Chiroma ya ce, sun binciki yaron ba a cire komai na jikinsa ba, amma suna zargin ɓata garin jininsa suka tatsa.

A wani mai kama da wannan, ranar Asabar wasu ɓata gari sun rataye wata yarinya Fatima Sule ƴar shekaru 13 a jikin taga a unguwar Dandishe Yamma layin Malam Kamalu da ke Karamar Hukumar Dala a Kanon.

Rahotonnin da Arewa Updates ta samu sun nuna cewa lamarin ya faru ne a lokacin da mahaifiyar yarinyar ta tafi unguwa, amma da dawowarta ta tarar da ita rataye a mace.

vanguard newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp