fidelitybank

Ingila ta fitar da jerin ‘yan wasa 26 da za su je Qatar

Date:

An saka dan wasan tsakiya na Leicester James Maddison a cikin ‘yan wasa 26 da Ingila za ta wakilci kasar a gasar cin kofin duniya da za a yi a Qatar.

Mai horaswa Gareth Southgate, ya kuma zabo dan wasan gaban Manchester United Marcus Rashford da dan wasan Newcastle Callum Wilson da dan wasan baya na Manchester City Kyle Walker da kuma dan bayan Arsenal Ben White.

Amma dan wasan baya na AC Milan Fikayo Tomori da dan wasan Brentford Ivan Toney da dan wasan gaba na West Ham Jarrod Bowen ba su samu ba.

Ingila za ta kara da Iran a gasar cin kofin duniya ranar 21 ga watan Nuwamba agogon (13:00 GMT).

Wales da Amurka ne ke hade da su a rukunin B.

Dan wasan tsakiya na Manchester City Kalvin Phillips, duk da cewa ya dawo daga hutun watanni biyu yana fama da matsalar kafadarsa, hakama Harry Maguire na tsakiya, wanda yasha wahala wajen samun wasa a Manchester United a kakar wasa ta bana.

Sai dai abokin wasan Maguire Jadon Sancho bai shiga cikin tawagar ba.

Zabi tawagar ku ta Ingila a gasar cin kofin duniya
Shearer ya yi hasashen fitar Ingila wasan daf da na kusa da karshe
tawagar Ingila
Masu tsaron gida: Jordan Pickford (Everton), Nick Pope (Newcastle), Aaron Ramsdale (Arsenal)

Masu tsaron baya: Harry Maguire (Manchester United), Luke Shaw (Manchester United), Eric Dier (Tottenham), John Stones (Manchester City), Kyle Walker (Manchester City), Kieran Trippier (Newcastle), Conor Coady (Everton), Ben White (Arsenal), Trent Alexander-Arnold (Liverpool)

‘Yan wasan tsakiya: Jude Bellingham (Borussia Dortmund), Mason Mount (Chelsea), Conor Gallagher (Chelsea), Declan Rice (West Ham), Jordan Henderson (Liverpool), Kalvin Phillips (Manchester City)

‘Yan wasan gaba: James Maddison (Leicester), Phil Foden (Manchester City), Jack Grealish (Manchester City), Harry Kane (Tottenham), Bukayo Saka (Arsenal), Raheem Sterling (Chelsea), Callum Wilson (Newcastle), Marcus Rashford (Manchester). United)

legit.ng.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a Æ™yale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp