Majalisar zartaswa ta tarayya ta amince da sake duba tare da inganta albashin ‘yan sanda da kashi 20 cikin 100.
Ministan harkokin ‘yan sanda, Maigari Dingyadi ne ya bayyana hakan a ranar Laraba, bayan kammala taron majalisar zartarwa na tarayya wanda shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya jagoranta a sabbin zaurukan majalisar da a ka yi wa kwaskwarima.
A cewar ministan,”A na sa ran aikin bitar zai fara aiki daga watan Janairun 2022. Wannan bita ya biyo bayan bukatun da masu zanga-zangar EndSARS su ka gabatar a shekarar 2020, wanda ya shafi inganta jin dadin jami’an ‘yan sanda”.
Ya ci gaba da cewa,”Za a kara albashin daukar gida ne ta hanyar alawus din yawon bude ido zuwa kashi 6 cikin 100 na sabon albashin da za su tafi gida da kuma amincewa da Naira biliyan 1.12 domin biyan wasu fa’idodin da ba su da inshora a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2020”. Inji Maigari.
Shugaba Buhari ya yi alkawarin cewa za a inganta albashin daidai da yadda a ke yi domin ci gaba da wanzar da zaman lafiya a kasar.
Zauren majalisar ya kuma amince da fitar da Naira biliyan 13.1 donmi biyan wasu fa’idodin mutuwa na ma’aikata 5,472 na tsawon lokacin rashin inshora na 2013 zuwa Agusta 2021.