fidelitybank

Inganta albashin ‘Yan sanda: Majalisa ta amince da karin albashin su

Date:

Majalisar zartaswa ta tarayya ta amince da sake duba tare da inganta albashin ‘yan sanda da kashi 20 cikin 100.

Ministan harkokin ‘yan sanda, Maigari Dingyadi ne ya bayyana hakan a ranar Laraba, bayan kammala taron majalisar zartarwa na tarayya wanda shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya jagoranta a sabbin zaurukan majalisar da a ka yi wa kwaskwarima.

A cewar ministan,”A na sa ran aikin bitar zai fara aiki daga watan Janairun 2022. Wannan bita ya biyo bayan bukatun da masu zanga-zangar EndSARS su ka gabatar a shekarar 2020, wanda ya shafi inganta jin dadin jami’an ‘yan sanda”.

Ya ci gaba da cewa,”Za a kara albashin daukar gida ne ta hanyar alawus din yawon bude ido zuwa kashi 6 cikin 100 na sabon albashin da za su tafi gida da kuma amincewa da Naira biliyan 1.12 domin biyan wasu fa’idodin da ba su da inshora a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2020”. Inji Maigari.

Shugaba Buhari ya yi alkawarin cewa za a inganta albashin daidai da yadda a ke yi domin ci gaba da wanzar da zaman lafiya a kasar.

Zauren majalisar ya kuma amince da fitar da Naira biliyan 13.1 donmi biyan wasu fa’idodin mutuwa na ma’aikata 5,472 na tsawon lokacin rashin inshora na 2013 zuwa Agusta 2021.

 

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp