fidelitybank

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

Date:

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya na shekarar 2027, hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC) ta bayyana shirin ta na fitar da ƙarin ƙa’idoji da za su jagoranci yadda za a duba sakamakon zaɓe da aka riga aka bayyana.

Shugaban INEC, farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan a taron kwata na biyu da kwamishinonin zaɓe na jihohi (RECs) a Abuja .

Ya jaddada cewa kwamishinonin zaɓe su ɗauki cikakken nauyin aikinsu bisa ƙundin tsarin mulki.

Farfesa Yakubu ya kuma bayyana damuwa kan yadda mutane ke fassara Sashe na 65 na dokar zaɓe ta 2022 .wadda ke ba INEC damar duba sakamakon zaɓe ta hanyoyi daban-daban, inda ya ce hukumar na aiki kan sabbin ƙa’idoji da za su bayyana yadda ake nazari da sake duba sakamakon zaɓe.

“Sabbin dokokin za su kasance ƙari ne ga dokokin gudanar da zaɓe na 2022, kuma za a wallafa su a shafin hukumar nan bada jimawa.” shugaban hukumar ya ƙara da cewa.

Ya kara da cewa INEC ta riga ta gana da shugabannin jam’iyyu da ƙungiyoyin fararen hula da ‘yan jarida da jami’an tsaro domin samun haɗin kai.

Haka kuma, dukkan jihohin Najeriya da Abuja sun riga suna da sabbin kwamishinonin zaɓe (RECs) masu cikakken iko.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Peter Obi ka gaggauta ficewa daga jam’iyyar mu nan da awa 48 – Labour Party

Bangaren jam’iyyar Labour da Julius Abure ke jagoranta, ya...

Lakurawa sun kashe Mutane 15 a Sokoto

Wasu da ake zargin mambobin ƙungiyar Lakurawa ne sun...

Dan wasan Liverpool Diago Jota da Kaninsa sun mu a hadarin mota

Ɗan wasan ƙwallon ƙafar Liverpool kuma ɗan ƙasar Portugal,...

Mun shirya tunkarar APC a 2027 – ADC

A ranar Laraba ne manyan ƴan adawar siyasa suka...

Mun dagulawa Iran lisafi na tsawon shekaru biyu a nukiliyar ta – Amurka

Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce bayannan leken asirinta ya...

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya...

Isra’ila ta amince da sharuɗɗan yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce Isra'ila ta amince...

Buhari ba zai taɓa cin amanar Tinubu ba – Garba Shehu

Tsohon babban mataimaki na musamman kan harkokin yada labarai...

Mutane 207 ne suka mutu a ambaliyar Neja – NSEMA

Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta...

Jiga-jigan jam’iyyar PDP za su sauya sheƙa don tunkarar APC a 2027

Wasu jiga-jigan jam'iyyar PDP da suka hada da tsohon...

Za a ƙaddamar da jam’iyyar hammaya da za ta tunkari APC

Gamayyar jam'iyyun adawa a ranar Talata, ta amince da...

Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram Takwas a jihar Borno

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta sun kashe aƙalla...
X whatsapp