fidelitybank

INEC za ta fitar da sabbin ƙa’idojin duba sakamakon zaɓe

Date:

A shirye-shiryen da take yi gabanin babban zaɓen Najeriya na shekarar 2027, hukumar zaɓe ta ƙasa (INEC) ta bayyana shirin ta na fitar da ƙarin ƙa’idoji da za su jagoranci yadda za a duba sakamakon zaɓe da aka riga aka bayyana.

Shugaban INEC, farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan a taron kwata na biyu da kwamishinonin zaɓe na jihohi (RECs) a Abuja .

Ya jaddada cewa kwamishinonin zaɓe su ɗauki cikakken nauyin aikinsu bisa ƙundin tsarin mulki.

Farfesa Yakubu ya kuma bayyana damuwa kan yadda mutane ke fassara Sashe na 65 na dokar zaɓe ta 2022 .wadda ke ba INEC damar duba sakamakon zaɓe ta hanyoyi daban-daban, inda ya ce hukumar na aiki kan sabbin ƙa’idoji da za su bayyana yadda ake nazari da sake duba sakamakon zaɓe.

“Sabbin dokokin za su kasance ƙari ne ga dokokin gudanar da zaɓe na 2022, kuma za a wallafa su a shafin hukumar nan bada jimawa.” shugaban hukumar ya ƙara da cewa.

Ya kara da cewa INEC ta riga ta gana da shugabannin jam’iyyu da ƙungiyoyin fararen hula da ‘yan jarida da jami’an tsaro domin samun haɗin kai.

Haka kuma, dukkan jihohin Najeriya da Abuja sun riga suna da sabbin kwamishinonin zaɓe (RECs) masu cikakken iko.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp