Shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa INEC, Farfesa Mahmud Yakubu, ya ce, hukumar za ta bi duk wani umarnin kotu game da rushe ko yi wa jam’iyyun siyasa rajista a ƙasar.
Farfesa Yakubu ya bayyana hakan ne a yau Asabar yayin wani taron ƙara wa juna sani da ke gudana yanzu haka a Abuja game da babban zaɓen ƙasar da ke tafe a 2023.
Tun a watan Fabarairu na 2020 ne INEC ta soke jam’iyyun siyasa 74 a Najeriya, abin da ya hana su shiga duk wani zaɓe da za a gudanar a ƙasar. In ji BBC.
Da aka tambaye shi game da dalilin da ya sa INEC ta soke rajistar jam’iyyar Youth Party (YP) duk da umarnin kotu, shugaban hukumar ya ce har yanzu batun yana kotu.
“Jam’iyya 74 abin ya shafa kuma YP na cikinsu,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa “zamu yi biyayya ga umarnin kotu da zarar mun samu”. In ji Yakubu.