fidelitybank

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Date:

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana haka ranar Juma’a yayin da ya karɓi baƙuncin shugaban hukumar kula da gidajen yari na ƙasar, Sylvester Ndidi Nwakuche Ofori, da ya buƙaci hakan.

Mista Ofori ya ce ya kamata hukumar ta duba wannan buƙata tasa saboda su ma ɗaurarru suna da ƴancin zaɓe a ƙarƙashin dokokin Najeriya.

“Kowa zai iya samun kansa a wannan yanayi, idan ya saɓa doka, don haka ya kamata mu duba yadda kula da su, suna da ƴancin da doka ta ba su, ɗaya daga cikin ƴancin kuwa shi ne ƴancin kaɗa ƙuri’a. Kasancewarsu a kurkuku ba zai janye musu ƴancinsu na zaɓe ba,” in ji Mista Ofori.

Shugaban hukumar kula da gidajen yarin ya ce akwai ɗaurarru fiye da 81,000 a faɗin gidajen yarin ƙasar, kuma kusan kashi 66 daga cikinsu na zaman jiran shari’a ne.

Hukunce-hukunce kotuna a 2014 da 2018 sun tabatar da hukuncin bai wa ɗaurarrau damar kaɗa ƙuri’unsu a zaɓukan ƙasar.

Shugaban hukumar zaɓenya ce INEC ta yi jerin ganawa da hukumar kula da gidajen yarin domin tsara yadda ɗaurarrun za su kaɗa ƙuri’ar tasu, ciki har da samun damar zuwa inda suke ɗaure domin ba su damar jefa ƙuri’a.

Haka kuma shugaban na INEC ya nemi ɗaukin majalisar dokokin ƙasar domin tabbatar da ƙudurin.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp