fidelitybank

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Date:

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana haka ranar Juma’a yayin da ya karɓi baƙuncin shugaban hukumar kula da gidajen yari na ƙasar, Sylvester Ndidi Nwakuche Ofori, da ya buƙaci hakan.

Mista Ofori ya ce ya kamata hukumar ta duba wannan buƙata tasa saboda su ma ɗaurarru suna da ƴancin zaɓe a ƙarƙashin dokokin Najeriya.

“Kowa zai iya samun kansa a wannan yanayi, idan ya saɓa doka, don haka ya kamata mu duba yadda kula da su, suna da ƴancin da doka ta ba su, ɗaya daga cikin ƴancin kuwa shi ne ƴancin kaɗa ƙuri’a. Kasancewarsu a kurkuku ba zai janye musu ƴancinsu na zaɓe ba,” in ji Mista Ofori.

Shugaban hukumar kula da gidajen yarin ya ce akwai ɗaurarru fiye da 81,000 a faɗin gidajen yarin ƙasar, kuma kusan kashi 66 daga cikinsu na zaman jiran shari’a ne.

Hukunce-hukunce kotuna a 2014 da 2018 sun tabatar da hukuncin bai wa ɗaurarrau damar kaɗa ƙuri’unsu a zaɓukan ƙasar.

Shugaban hukumar zaɓenya ce INEC ta yi jerin ganawa da hukumar kula da gidajen yarin domin tsara yadda ɗaurarrun za su kaɗa ƙuri’ar tasu, ciki har da samun damar zuwa inda suke ɗaure domin ba su damar jefa ƙuri’a.

Haka kuma shugaban na INEC ya nemi ɗaukin majalisar dokokin ƙasar domin tabbatar da ƙudurin.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp