fidelitybank

INEC ta wallafa sunan Machina dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa

Date:

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta wallafa sunan Bashir Machina a shafinta na yanar gizo a matsayin dan takarar Sanatan Yobe ta Arewa.

Wannan dai ya yi daidai da wata wasika da hedikwatar jam’iyyar APC ta kasa ta aikewa alkalan zaben, inda ta bukaci ta karba tare da buga sunan Machina a matsayin dan takarar kujerar Sanata na jam’iyyar.

Husaini Mohammed Isa, kakakin kungiyar yakin neman zaben Machina ne ya tabbatar da hakan a wani sako da ya wallafa a dandalin sada zumunta a ranar Juma’a.

“INEC Ta Buga Sunan Machina A Portal Ta A Matsayin Dan Takarar Sanatan APC na Yobe ta Arewa.

“Hukumar zabe mai zaman kanta ta yi biyayya ga wasikar da jam’iyyar APC ta rubuta wa Umpire na neman hukumar zabe ta amince da buga sunan Bashir Machina a matsayin dan takararta na Sanatan Yobe ta Arewa,” inji shi.

Idan ba a manta ba, wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Damaturu, ta yanke hukuncin daurin rai-da-rai ga INEC da APC da su amince da Bashir Machina a matsayin dan takarar sanata na jam’iyyar a Yobe ta Arewa.

Wannan ci gaban ya haifar da hasashe kan ko Jam’iyyar za ta bi umarnin kotu da kotun ta ba ta.

Bashir Machina na fatan maye gurbin shugaban majalisar dattawa mai ci, Ahmad Ibrahim Lawan a majalisa ta 10 idan har aka zabe shi a matsayin Sanata mai wakiltar Yobe ta Arewa.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaĈ™i da fataucin miyagun Ĉ™wayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun Ĉ™wayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miĈ™a saĈ™on ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaĈ™alar belin Danwawu,...
X whatsapp