Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, INEC, a karshen mako ta ce, za ta fara gabatar da takardun shaidar cin zabe ga zababbun ‘yan majalisar dokokin kasar a ranar Talata.
Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana haka a lokacin wani taro da hukumar zabe ta Resident Electoral Commissions (RECs) a Abuja ranar Asabar.
Yakubu ya bayyana cewa za a gabatar da zababbun ‘yan majalisar wakilai satifiket din su ranar Laraba, yayin da zababbun sanatoci kuma za su karbi nasu ranar Talata.
Shugaban na INEC ya ce: “Duk da haka, don gudanar da ingantaccen taron jama’a, kowane Sanata/Zaɓaɓɓen Memba ya kamata ya kasance tare da mafi yawan baƙi biyu.
“Za a loda cikakken jerin sunayen membobin da aka zaba zuwa gidan yanar gizon Hukumar nan ba da jimawa ba.”