fidelitybank

INEC ta tsayar da ranar Asabar a matsayin ranar ƙarasa zaɓe a wasu jihohi

Date:

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta INEC, ta sanya Asabar 15 ga watan Afrilu a matsayin ranar ƙarasa zaɓukan da ba su kammala ba a jihohi da dama na ƙasar nan.

A wani saƙo da ta wallafa a shafinta na Twitter ranar Litinin, INEC ta ce, ta yanke wannan shawara ce, bayan wata ganawa tsakanin manyan jami’anta.

Akwai zaɓukan gwamnoni kamar a jihohin Kebbi da Adamawa, waɗanda jami’an sanar da sakamakon zaɓe suka ce ba su kammala ba a ranar 18 ga watan Maris, baya ga sauran zaɓukan ‘yan majalisun dokoki, da su ma suka fuskanci irin wannan cikas.

Ɗaya daga cikin jihohi da aka samu zaɓukan da ba su kammala ba masu yawa a ranar 25 ga watan Fabrairu, ita ce Sokoto, inda ake da ‘yan majalisar wakilai 11 da sanatoci 3 waɗanda duk zaɓensu bai kammalu ba.

Masu sa-ido sun soki hukumar INEC saboda matsalolin da aka samu a zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya na ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu, wanda Bola Ahmed Tinubu, ya yi nasarar zama sabon shugaban ƙasa.

Haka ma a ranar 18 ga watan Maris lokacin da INEC ta gudanar da zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar dokokin jihohi, an gamu da wasu daga cikin matsalolin da aka samu a zaɓen INEC na farko

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...
X whatsapp