fidelitybank

INEC ta tsawaita wa’adin karbar katin zabe

Date:

Hukumar zaɓe ta INEC, ta tsawaita wa’adin karɓar katin zaɓe da take rabawa a faɗin ƙasar da kwana takwas.

Shugaban Sashen Yaɗa Labarai na Inec Festus Okoye ya ce an ɗauki matakin ne don bai wa masu kaɗa ƙuri’a isasshen lokaci na karɓar katin kafin fara jefa ƙuri’a a babban zaɓe na 2023.

“Saboda wannan dalilin, an tsawaita wa’adin karɓar katin zaɓen da kwana takwas,” in ji shi. “A madadin wa’adin ya ƙare ranar Lahadi, 22 ga watan Janairu, za a ci gaba da karɓa har zuwa Lahadi, 29 ga wata.”

Inec ta ce lokacin karɓar katin shi ne 9:00 na safe zuwa 3:00 na rana a kowace rana – har Asabar da Lahadi.

Kazalika, tsawaitawar ta shafi dukkan matakan raba katin na ƙaramar hukumar da kuma mazaɓa.

A ranar 25 ga watan Fabarairu ne za a fara kaɗa ƙuri’a, inda ake sa ran ‘yan Najeriya miliyan 93.4 da ke da rajistar zaɓen za su zaɓi shugaban ƙasa da ‘yan majalisar tarayya. Sai kuma gwamnoni da ‘yan majalisar jiha da za a zaɓa a watan Maris.

natforce 
latest news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...

Majalisar Dinkin Duniya za ta dakatar da tallafin abinci a Najeriya

Shirin Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana...

Tinubu ya na murkushe ‘Yan adawa – Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya ce...

Gwamnatin Kano ta baiwa yara fifiko – UNICEF

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya...

Majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 21

A ranar Talata ne majalisar Dattawa ta amince da...

An sallami Gwamnan Katsina daga asibiti bayan ya samu rauni a hatsarin mota

An sallami gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda,...

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...

An fara samun takun saka tsakanin Turkiyya da Najeriya a kan kungiyar Gulen

Kungiyar kare hakkin musulmi, MURIC, ta bukaci shugaban kasar...

Arziƙin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 a farkon 2025 – NBS

Tattalin arzikin Najeriya ya ƙaru da kashi 3.13 cikin...

Kamfanonin lantarki za su katse wutar lantarki saboda bashi

Kamfanonin samar da wutar lantarki, sun ce suna iya...
X whatsapp