A jihar Bayelsa da ke kudancin Najeriya, hukumar zaɓe ta ƙasa National Independent Eloctoral Commission (INEC), ta tabbatar da hatsarin da wani jirgin ruwa ya yi lokacin da yake jigilar jami’anta.
Jirgin na kan hanyarsa ta zuwa rumfar zaɓe ta 17 a Koluama da ke ƙaramar hukumar Ijawa ta kudu ɗauke da kayayyakin zaɓe masu muhimmanci.
Shugaban sashen wayar da kan masu kaɗa ƙuri’a na Inec a jihar Bayelsa, Wilfred O. Ifodah, ya ce an ceto dukkan jami’ai 12 da ke cikin jirgin.
Sai dai ya ce akwai kayan aikin zaɓe da suka ɓace, waɗanda suka haɗa da takardar rubuta sakamakon zaɓe, da na’urorin cajin batirin kwamfutar aikin zaɓen, da kuma wasu kayyayakin.
Sanarwar da Inec ta fitar ta ce masu zaɓe 5,368 ne suka yi rijista a yankin, kuma 5,311 sun karɓi katin zaɓensu.
Inec ta ce tana bakin ƙoƙarinta don ganin an gudanar da zaɓe a yankin lami lafiya