fidelitybank

INEC ta magantu a kan katunan zaben da aka binne a Imo

Date:

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta mayar da martani kan wani hoton bidiyo na binne katunan zabe na dindindin, PVC a jihar Imo.

Hukumar a cikin wata sanarwa da kwamishinanta na kasa Festus ya fitar, ta ce ta fara gudanar da bincike cikin gaggawa kuma duk wanda aka samu da laifin aikata hakan za a hukunta shi a karkashin doka.

“An jawo hankalin Hukumar kan faifan bidiyo da ke yawo a yanar gizo na katin zabe na dindindin (PVCs) da ake zargin an binne a karkashin kasa a wasu wurare, ciki har da harabar wani babban kamfani.

“Hukumar ba ta daukar wadannan zarge-zarge da wasa. Mun fara gudanar da bincike cikin gaggawa kuma duk wanda aka samu da laifi a cikin wannan makircin a fili yana da niyyar bata wa ‘yan Najeriya hakkinsa za a hukunta shi a karkashin doka. Duk dan Najeriya da ya cancanta da ya yi rajista a matsayin mai jefa kuri’a, yana da hakkin ya sami katunan zaben.

“Bai kamata a tauye ‘yancin kada kuri’a a kowane zabe ba ko kuma a tauye hakkin tsarin mulki ta kowace hanya.

“Game da tarihin hukumar, an buga katin zabe na PVC ga duk masu rajista a Najeriya har zuwa ranar 14 ga watan Janairun 2022 kuma an kai su ga dukkan jihohin tarayya domin karban masu zabe.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaÉ“en 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin É—an kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp