Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta mayar da martani kan wani hoton bidiyo na binne katunan zabe na dindindin, PVC a jihar Imo.
Hukumar a cikin wata sanarwa da kwamishinanta na kasa Festus ya fitar, ta ce ta fara gudanar da bincike cikin gaggawa kuma duk wanda aka samu da laifin aikata hakan za a hukunta shi a karkashin doka.
“An jawo hankalin Hukumar kan faifan bidiyo da ke yawo a yanar gizo na katin zabe na dindindin (PVCs) da ake zargin an binne a karkashin kasa a wasu wurare, ciki har da harabar wani babban kamfani.
“Hukumar ba ta daukar wadannan zarge-zarge da wasa. Mun fara gudanar da bincike cikin gaggawa kuma duk wanda aka samu da laifi a cikin wannan makircin a fili yana da niyyar bata wa ‘yan Najeriya hakkinsa za a hukunta shi a karkashin doka. Duk dan Najeriya da ya cancanta da ya yi rajista a matsayin mai jefa kuri’a, yana da hakkin ya sami katunan zaben.
“Bai kamata a tauye ‘yancin kada kuri’a a kowane zabe ba ko kuma a tauye hakkin tsarin mulki ta kowace hanya.
“Game da tarihin hukumar, an buga katin zabe na PVC ga duk masu rajista a Najeriya har zuwa ranar 14 ga watan Janairun 2022 kuma an kai su ga dukkan jihohin tarayya domin karban masu zabe.