Hukumar Zaben mai zaman kanta ta kasa, INEC, ta ce, ta kwashe kayan zabe masu muhimmanci daga ofishinta na jihar Imo sakamakon hari tare da lalata kayan da ke ciki, a yankin ƙaramar hukumar Isu.
Shugaban sashen wayar da kan masu zabe da yada labarai na hukumar ta INEC Festus Okoye, ne ya bayyana hakan a ranar Larabar a Abuja.
“Saboda haka ne muka ɗauki matakan bai wa kayan zaben kariya, inda muka canza wa kayan zabe mazauni,” in ji shi.
Ya kara da cewa: “Haka zalika dukkan katin zaben da ba a karɓa ba, muna adanawa, sannan za a ƙaro jami’an tsaron don tabbbatar da an ci gaba da aikin rarraba katin ga masu shi, a harabar ofishin.”
Festus Okoye ya ce wannan shi ne karo na huɗu da aka kai hari ofishin INEC a jihar Imo da ke kudancin Najeriya, a ƙasa da makonni uku, bayan da aka kai makamancin wannan hari a ƙaramar hukumar Orlu da Oru dukkan su a jihar ta Imo.