fidelitybank

INEC ta kulla yarjejeniya da masu motar haya da jirgin ruwa

Date:

Hukumar zabe mai zaman kanta INEC, ta kullu wata yarjejeniya tsakaninta da kungiyar motocin haya da masu motocin da na jiragen ruwa, kan yadda za su yi jigila da ma’aikatan hukumar da kuma kayayyakin zabe a lokutan zaben 2023.

Yarjejeniyar za ta mayar da hankali kan rawar da sufuri zai taka a zabukan da za a gudanar a Najeriya a shekara mai zuwa.

A bangare guda kuma, Tarayyar Turai ta ce za ta aike da masu sa ido kan zaben da aka shirya gudanarwa a ranakun 25 ga watan Fabrairu da kuma na 11 ga watan Maris din 2023.

Yarjejeniyar an kullata ne domin ganin yadda za a kai mambobi da kuma kayayyakin aikin zaben wuraren zaben a kan lokaci kuma cikin aminci.

A yayin kulla wannan yarjejeniya, shugaban hukumar Farfesa Mahmood Yakubu, ya ce suna bukatar manyan motoci na haya da kanana har ma da jiragen ruwa domin kai wa ga garuruwan da ke kan hayi.

A cewarsa akwai bukatar mutane sama da miliyan daya da za su yi aikin da motoci sama da 100,000 da jiragen ruwa 4,200 domin yin jigilar kayayyakin aiki zuwa rumfunan zabe 176,846 a mazabu 8,809 cikin kananan hukumomi 774 na jihohin kasar 36.

Irin wannan yarjejeniya aka cimma a ranar 12 ga watan Disambar 2018, domin gudanar da zaben 2019 wanda a cewar shugaban hukumar, nasarar da aka samu ta gudanar da zaben lafiya ta sa aka kara karfafa amfani da hanyar sufurin.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp